KatsinaTimes | 24 ga Maris, 2026
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta kammala shirye-shiryen gudanar da babban taronta na ƙasa da za a yi ranar Asabar a filin Eagle Square da ke Abuja, inda ake sa ran wakilai akalla 7,200 daga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya (FCT) za su halarta.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, tare da shugaban kwamitin tsare-tsaren babban taron na 2026 kuma tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, sun tabbatar wa mambobin jam’iyyar cewa taron zai gudana cikin nasara ba tare da tangarda ba.
A yayin wani tattaki da aka gudanar mai taken “Tafiya don tsafta da muhalli mai kyau” da ƙaramin kwamitin tsafta da muhalli na taron ya shirya, Yilwatda, wanda Mataimakin Sakataren Shirye-shiryen Jam’iyya na Ƙasa, Nze Chidi Duru ya wakilta, ya ce jam’iyyar ta shirya tsaf domin gudanar da taron.
“Mun shirya, kuma muna fatan ranar Asabar za ta zo domin gudanar da wannan taro. Ba wai taro kawai muke shiryawa ba, muna kuma shirin zaben fidda gwani,” in ji shi, yana mai ƙara da cewa duk wata matsala za a shawo kanta.
Shi ma Masari ya nuna gamsuwa da yadda aka shirya taron, yana mai cewa ko da akwai ƙalubale kaɗan, ba za su hana gudanar da taron yadda ya kamata ba.
“Mun shirya. Taron zai gudana kamar yadda aka tsara,” in ji shi.
Mataimakin shugaban kwamitin tsafta da muhalli kuma tsohon gwamnan jihar Cross River, Ben Ayade, ya ce jam’iyyar ta nuna ƙarfin da take da shi wajen shirya babban taro cikin lumana da nasara. Ya ƙara da cewa APC na sake tsara kanta domin tunkarar zaɓe masu zuwa.
Haka zalika, sakatariyar kwamitin, Sanata Uche Ekwunife, ta bayyana cewa jam’iyyar ba ta shirya taron kaɗai ba, har ma da zaɓen shekarar 2027, tana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa za su ci gaba da mulki a matakin tarayya.
A nasa ɓangaren, mataimakin shugaban kwamitin tsare-tsaren taron kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, Anyim Pius Anyim, ya tabbatar da cewa za su gudanar da taron fiye da yadda jama’a ke tsammani.
Tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya ce gyare-gyaren da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa za su haifar da alheri, yana mai kira ga ‘yan Najeriya da su yi haƙuri.
Ya ƙara da cewa taron na ba jam’iyyar damar gabatar da ayyukanta da kuma yin hulɗa da jama’a gabanin zaɓen gaba.
Kwamitin tantance ‘yan takara ya yi alƙawarin adalci
A gabanin taron, shugaban kwamitin tantance masu neman mukaman jam’iyya kuma gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya yi alƙawarin gudanar da sahihin aiki cikin gaskiya da adalci.
Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin a Abuja, Oyebanji ya ce za su bi kundin tsarin mulkin jam’iyya da dokar zaɓe wajen gudanar da aikin.
“Za mu yi aiki cikin gaskiya, adalci da nuna gaskiya ga kowa. Ba za a nuna wariya ba,” in ji shi.
Mataimakin sakataren kwamitin, Philip Shaibu, ya bayyana cewa za su tantance ‘yan takara kusan 30, tare da tsara aikin yadda zai gudana cikin sauƙi cikin ɗan gajeren lokaci.
Shi ma mataimakin shugaban kwamitin, gwamnan jihar Kogi Ahmed Ododo, ya ce aikin tantancewar wata muhimmiyar gwaji ce ga dimokuraɗiyyar cikin gida ta jam’iyyar, yana mai cewa sakamakon zai taimaka wajen gina makomar APC.
Zaɓen Tinubu a 2027 ‘tabbas ne’ — Kalu
A wani ɓangare, mataimakin kakakin majalisar wakilai, Benjamin Kalu, ya bayyana cewa babu wanda zai hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu sake lashe zaɓe a shekarar 2027.
Kalu, wanda ya yi wannan bayani yayin karɓar shugabannin ƙungiyar City Boy Movement na jihar Abia, ya ce nasarorin gwamnati da bai wa matasa dama su ne za su tabbatar da nasara.
Ya bayyana Tinubu a matsayin shugaba mai goyon bayan matasa, yana mai cewa yana ƙoƙarin gina sabbin shugabanni na gaba.
Kalu ya kuma ce dandalinsa na Renewed Hope Partners zai ci gaba da yaɗa ayyukan gwamnati da kuma tara goyon bayan jama’a a sassan ƙasa.